An Kama Wani Saurayi Kan Zargin Yin Ajalin Budurwarsa A Kaduna



Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna ta kama wani mutum, Manaseh Jatau, bisa zargin kashe budurwarsa mai shekaru 35, Rebecca Jeremiah, bayan wata takaddama da ta samo asali daga kiran waya da wata mata ta yi masa.

An gano gawar Jeremiah a kan titin Mai Angwa da ke Romi, Kaduna, da misalin karfe 7 na safe ranar Asabar, 5 ga Satumba, 2026.

Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, Mansir Hassan, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Hassan ya ce jami’in da ke kula da ofishin ‘yan sanda na Romi ne ya kai rahoton gano gawar, bayan haka jami’an bincike suka garzaya wurin.

Daga nan jami’an suka garzaya da Jeremiah zuwa asibitin St Gerald da ke Kakuri, Kaduna, inda likita ya tabbatar da mutuwarta. An kuma ajiye gawarta a dakin adana gawa domin gudanar da binciken gawar.

Binciken farko ya nuna cewa Jatau ne mutum na karshe da ya tuntubi Jeremiah, kuma shi ne ya gayyace ta zuwa Ebano Joint da ke Romi.

A cewar rundunar, Jatau ya amsa cewa sun yi fada a dakinsa kan kiran waya da wata mata ta yi masa, lamarin da ake zargin ya kai ga mutuwar Jeremiah.

Hassan ya kara da cewa wanda ake zargin ya amsa cewa ya jefar da gawar Jeremiah a wani fili da ke kusa da gidansa domin boye abin da ya faru.

Jatau na tsare a hannun ‘yan sanda yayin da jami’an bincike ke ci gaba da gudanar da bincike kan musabbabin mutuwar matar.

Rundunar ta ce za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

#TheSardaunaTV

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...