
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Ogun ta kama wasu mata uku da ake zargi da hannu a wata kungiyar satar yara a Ibafo, karamar hukumar Obafemi Owode ta jihar.
Jami’an sashen bincike na rundunar ‘yan sandan Ibafo ne suka kama wadanda ake zargin bayan gudanar da bincike bisa bayanan sirri kan rahoton satar yara.
Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, Oluseyi Babaseyi, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na X ranar Juma’a.
Rundunar ta bayyana wadanda aka kama da suka hada da Kikelomo Jimoh, mai shekaru 36, Kayode Elizabeth da Blessing Anochike, mai shekaru 60. Ta ce an kuma ceto yara uku da lamarin ya shafa.
Binciken farko ya nuna cewa yaran da aka ceto su ne Christiana Olowokere, ‘F’, mai shekaru 14; Olamilekan Abdurusheed, ‘M’, mai shekaru 16; da Adeniji Rebecca, ‘F’, mai shekaru 12.
A cewar ‘yan sandan, ana zargin an sayar da Christiana kan N500,000, yayin da Olamilekan, wanda ya taba guduwa daga gidan iyayensa, aka yi zargin cewa an sace shi daga baya.
Haka kuma, rundunar ta ce har yanzu tana binciken yadda Adeniji Rebecca ta shiga hannun wadanda ake zargin da kuma yadda aka rika kula da ita.