
Mutane 12 sun rasa rayukansu, yayin da wasu biyu suka samu munanan raunuka sakamakon wani hatsarin mota da ya afku a kan hanyar Kaduna zuwa Kachia ta Jihar Kaduna.
Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) ta tabbatar da faruwar hatsarin, wanda ya rutsa da motoci biyu kirar Volkswagen Golf a kauyen Doka da ke Kudancin Kaduna.
Kwamandan FRSC na Jihar Kaduna, Andrew Paul Longkam, ya ce mutane 14 ne ke cikin motocin biyu a lokacin da hatsarin ya faru. Ya ce mutane 12 sun mutu, yayin da biyu suka tsira da raunuka masu tsanani.
Ya ce wadanda hatsarin ya rutsa da su sun kunshi maza takwas da mata shida. Dukkan mazan takwas da mata hudu sun mutu, yayin da sauran mata biyun suka tsira da raunuka.
Motocin da hatsarin ya rutsa da su sun hada da wata Volkswagen Golf mai launin shuɗi mai lambar rajista APP 394 FN, da kuma wata Volkswagen Golf ja mai lambar ACN 205 HK.
Longkam ya ce ana zargin fashewar tayar daya daga cikin motocin ce ta haddasa hatsarin.
Ya kuma bayyana cewa babu wani daga cikin mutanen da ke cikin motocin, har da direbobin biyu, da ya sanya bel din kujera ko amfani da wata na’urar kariya a lokacin hatsarin.
An kai wadanda suka tsira biyu zuwa Asibitin Rapha domin samun kulawar likitoci.
A halin yanzu, an kai gawarwakin wadanda suka mutu zuwa Babban Asibitin Idon, inda ake ajiye su yayin da ake kokarin gano wadanda suka mutu tare da tuntubar iyalansu.