
Rundunar ’Yan Sandan Najeriya ta gargadi jama’a kan yiwuwar kai hare-haren ta’addanci da aka shirya a makarantu, wuraren ibada, sansanonin horas da ’yan bautar ƙasa (NYSC) da sauran wuraren da ake ganin za su iya zama wuraren kai hari a faɗin ƙasar.
Gargadin ya biyo bayan samun bayanan sirri da ke nuna ƙara yawan motsin ’yan ta’adda da kuma sa ido da suke yi kan wuraren da za su iya kai wa hari, musamman yayin da ake shirin komawa zaman karatun shekarar 2026/2027.
A cikin wata sanarwar tsaro da aka aika wa rundunonin ’yan sanda a faɗin ƙasar, rundunar ta ce bayanan da Sashen Ayyuka ke da su sun nuna “an ƙara tattara ’yan ta’adda domin yiwuwar kai hare-haren hadin gwiwa” a wuraren da ke da rauni.
An aika sanarwar ga Mataimakan Sufeto-Janar na ’Yan Sanda da ke kula da shiyyoyin 1 zuwa 17, kwamishinonin ’yan sanda na jihohi, rundunonin Mobile Police, sassan yaƙi da ta’addanci da sauran sassan musamman.
Rundunar ta kuma ce ta samu rahoton motsin wasu ’yan bindiga daga Katsina ta Kaduna zuwa Jihar Filato.
’Yan sandan sun kuma bayyana cewa wasu da ake zargi da kasancewa ’yan ƙungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP), tare da wasu abokan hulɗarsu na cikin gida, suna gudanar da sa ido da bincike kan wuraren da ake shirin kai wa hari.
Rundunar ta bayyana barazanar da ke fuskantar makarantu a matsayin abin damuwa matuƙa, saboda yiwuwar kai hare-haren a daidai lokacin da makarantu ke komawa karatu.
Saboda haka, an umarci rundunonin ’yan sanda da abin ya shafa su ƙara tsaro a makarantu, wuraren ibada, sansanonin NYSC da sauran wuraren da ake ganin suna cikin haɗari.