
Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce ta kwato iko da sama da hekta 500,000 na filayen noma da ’yan bindiga suka mamaye a sassa daban-daban na jihar.
Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na jihar, Ahmed Maiyaki, ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin wani liyafar cin abinci da ma’aikatarsa ta shirya wa ’yan jarida na Kano Correspondents’ Chapel na Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ).
’Yan jaridar sun je Kaduna ne domin halartar taron bitarsu na shekarar 2026, wanda aka gudanar da taken “2027 General Elections: Navigating Legal, Security and Ethical Challenges in the Media.”
Maiyaki ya ce dawo da yankunan karkashin ikon gwamnati ya taimaka wajen inganta tsaro, tare da bai wa manoman da hare-haren ’yan bindiga suka hana zuwa gonakinsu damar komawa harkar noma.
Kwamishinan ya ce matsalar tsaro ta taba kawo cikas ga zirga-zirga tsakanin Kaduna da Abuja, inda wasu matafiya suka daina amfani da hanyar saboda hare-haren ’yan bindiga.
Sai dai ya ce yanzu lamarin ya sauya saboda an samu gagarumin ci gaba wajen tsaro a jihar.
Maiyaki ya jaddada cewa tsaro na daga cikin muhimman ginshikan shirin ci gaban gwamnatin jihar, domin ba za a samu ci gaban tattalin arziki da zamantakewa ba tare da ingantaccen tsaro ba.
Ya kuma bayyana wasu matakan da gwamnati ta dauka a bangaren noma, inda ya ce an raba tirelolin takin zamani guda 500 kyauta ga manoma sama da 150,000 a lokacin noman shekarar 2026.
A cewarsa, gwamnatin jihar ta raba tirelolin taki guda 400 kyauta ga manoma a shekarar 2024, sannan ta sake raba guda 500 a 2025.