Yan bindiga sun kashe fasinjojin wata motar haya a Jos



Aƙalla fasinjoji tara ne suka rasa rayukansu bayan ‘yan bindiga sun kai hari kan motar haya a Mahaɗar Dungus da ke Kuru a karamar hukuma Jos ta Kudu dake Jihar Filato. 

Mazauna yankin sun shaida wa ‘yan jarida cewa lamarin ya faru ne lokacin da direban motar ya tsaya domin sauke wasu fasinjoji a wurin. 

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa motar da ke kan hanyarta zuwa Jos ta kaca-kaca da jini kuma yin bulolin harsasai. 

Lawan Suleiman, malami kuma maƙwabcin ɗaya daga cikin waɗanda suka mutu, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa direban da aka kashe Ibrahim ne, wanda shi ɗalibinsa ne a baya. Ya ƙara da cewa uku daga cikin waɗanda aka kashe ‘yan unguwarsu ne a Bukuru, kuma gawarwakin an ajiye su a asibiti kafin a ɗauke su don jana’iza. 

Mai magana da yawun kungiyar matasan ta Berom Youth Moulders (BYM), Rwang Tengwong, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa fasinjojin na kan hanyarsu ta zuwa Jos ne lokacin da ‘yan ta’adda suka buɗe musu wuta. 

Ya ce: “Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:40 na dare. Dukkan waɗanda aka kashe fasinjoji ne da ke tafiya zuwa Jos. Daya daga cikin waɗanda aka kashe memba ne na Operation Rainbow. Wannan babban abun alhini ne kuma muna jimamin rasa rayuka.” 

A cewarsa, wasu daga cikin fasinjojin sun samu raunukan harbin bindiga kuma aka garzaya da su asibiti, inda wasu daga cikinsu suka mutu daga baya. 

Rundunar ‘yan sandan Jihar Filato ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da lamarin a lokacin da aka wallafa rahoton. 

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...