
Rundunar Sojin Najeriya ta sanar da kama wasu mutane shida da ake zargi da garkuwa da mutane a Jihar Adamawa, yayin da wani mayakin Boko Haram/ISWAP ya mika wuya ga jami’an tsaro a Jihar Borno.
Sojojin Operation Hadin Kai ne suka cafke wadanda ake zargin a yankin Soktu Hill da ke karamar hukumar Song ta Jihar Adamawa, bayan samun bayanan sirri kan ayyukan wata kungiyar masu garkuwa da mutane da ke aiki a yankin.
Mukaddashin Jami’in Yaɗa Labaran Sojojin Hadin Gwiwa na Arewa maso Gabas, Operation Hadin Kai, Kyaftin Mohammed Goni, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.
A cewar Goni, dakarun Sector 4 na Operation Hadin Kai tare da hadin gwiwar mafarauta na yankin sun kai samame maboyar kungiyar bayan samun sahihan bayanan sirri.
Samamen ya kai ga kama mutane uku da ake zargi da kasancewa cikin kungiyar, tare da kwato bindigar Dane guda.
Goni ya ce karin bincike da wasu ayyukan sirri da aka gudanar daga bisani sun kai ga kama wasu mutane uku, lamarin da ya sa adadin wadanda aka kama ya koma shida.
Ya bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa wadanda ake zargin sun dade suna gudanar da ayyukansu a yankunan Soktu, Dumne da Maigero na karamar hukumar Song.
A cewarsa, wadanda ake zargin sun amsa hannu wajen aikata wasu hare-haren garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa, baya ga wasu laifukan tashin hankali a yankin.
A Jihar Borno kuwa, Goni ya ce wani mayakin Boko Haram/ISWAP ya mika wuya ga sojoji a Borgozo, da ke karamar hukumar Kaga, ranar 13 ga Satumba, 2026.