Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya bai wa maniyyatan jihar da ke Saudiyya kyautar Riyal ɗari uku-uku yayin da ya kai musu ziyara a sansaninsu da ke Muna.
Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Malam Ibraheem Musa, ya fitar ta bayyana cewa kowanne maniyyaci zai samu kusan naira dubu ɗari da goma sha huɗu bisa farashin canji na yanzu.
Gwamnan ya yaba wa maniyyatan da hukumar jin daɗin Alhazai ta jihar Kaduna kan yadda aikin Hajjin bana ya gudana cikin nasara. Haka kuma ya jinjinawa kwamitin tawagar Hajji na jihar saboda gudanar da aikin cikin tsari.
Uba Sani ya kuma roƙi maniyyatan su yi addu’ar samun zaman lafiya a Najeriya, yana mai cewa ci gaba ba zai samu ba idan babu zaman lafiya.
A nasa jawabin, shugaban hukumar jin daɗin Alhazai ta Kaduna, Malam Salihu Abubakar, ya gode wa gwamnan bisa tallafin da yake bai wa hukumar domin sauƙaƙa aikin Hajji.
Uba Sani Ya Bai Wa Maniyyatan Kaduna Kyautar Riyal Ɗari Uku-uku

