
Rundunar tsaron sararin samaniyar Saudiyya ta ce ta kakkaɓo tare da lalata wani jirgin sama maras matuƙi da ƴan tawayen Houthi na Yemen suka harba zuwa yankin da ke kusa da birnin Makka mai tsarki.
A cewar ƙawancen sojojin da Saudiyya ke jagoranta a yaƙin Yemen, jirgin bai kai ga shiga yankin da aka haramta zirga-zirgar jiragen sama ba, yayin da ake ci gaba da fuskantar hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi a sassa daban-daban na ƙasar.
Mai magana da yawun ƙawancen, Turki al-Maliki, ya ce wannan shi ne karo na biyu da Houthi suka yi yunƙurin kai hari zuwa Makka.
Ya ce yunƙurin farko ya faru ne a watan Yulin 2017, lokacin da aka harba wani makami mai linzami mai cin dogon zango zuwa yankin.
A ranar Talata, 15 ga Satumba, hukumomin Saudiyya sun fitar da wani gargaɗin tsaro na ɗan lokaci a biranen Makka, Jiddah da Taif. Daga bisani, hukumomin tsaron farin kaya suka sanar da cewa an shawo kan barazanar kuma babu wata matsala da ta samu ga jama’a.
Gargaɗin da aka bayar a Makka ya haifar da fargaba a tsakanin mazauna birnin, musamman saboda ba kasafai ake samun irin wannan lamari a yankin ba a ‘yan kwanakin nan.
Kwana guda kafin hakan, ƙawancen ya ce hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi da Houthi suka kai kan biranen Saudiyya uku sun jikkata fararen hula 13.
Ƙawancen ya kuma ce hare-haren sun lalata gidaje bakwai da motoci biyu.
Ya zuwa yanzu, ƙungiyar Houthi ba ta fitar da wata sanarwa kan ikirarin da ƙawancen da Saudiyya ke jagoranta ya yi ba.