China Ta Ce Za Ta Kare Haƙƙoƙin Iran A Rikicin Gabas Ta Tsakiya



Ministan Harkokin Wajen China, Wang Yi, ya ce ƙasarsa na da niyyar kare haƙƙoƙi da buƙatun Iran a yayin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke ci gaba.

Wang ya bayyana hakan ne a wata ganawa da takwaransa na Iran, Abbas Araghchi, wanda ya kai ziyara China.

Ministan ya ce China a shirye take ta ƙara ƙarfafa tattaunawa da haɗin gwiwa da Iran, tare da kare haƙƙoƙi da buƙatun ƙasar.

China na daga cikin manyan abokan hulɗar tattalin arzikin Iran, kuma ta dade tana ƙoƙarin taimakawa wajen rage tasgaroƙin rikicin Gabas ta Tsakiya, wanda ya ɗauki tsawon watanni tare da bazuwa zuwa wasu ƙasashen makwabta da Iran.

A wani bangare kuma, an shirya Shugaban China, Xi Jinping, ya je Washington a makon gobe domin ganawa da Shugaban Amurka, Donald Trump.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...