
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi ikirarin cewa Iran ta sha kashi a yakin da ake yi, yana mai cewa kasar ta shiga cikin mawuyacin hali da ya raunana karfinta a fagen siyasar duniya.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya bayyana Iran a matsayin “kasa ce da ta gaza gaba daya”, inda ya ce kasar ba ta da karfin rundunar ruwa da ta sama, kudinta ya yi rauni, kuma tana fama da matsalar biyan jami’an tsaro albashi.
Ya kuma ce hauhawar farashi ya yi kamari a kasar, yayin da shugabannin Iran suka kasa wakiltar kasar yadda ya kamata.
Trump ya zargi gwamnatin Iran da amfani da karfi wajen murkushe masu zanga-zanga, inda ya ce an kashe mutane da dama.
A cewarsa, ya kamata a gurfanar da shugabannin Iran a gaban kotu bisa zargin aikata laifukan yaki da kuma cin zarafin bil’adama.