

Rundunar ƴan sandan jihar Kogi ta ce an samu nasarar kubutar da mutane 10 ƴan NYSC da yan bindiga su ka yi garkuwa da su.
Yan sandan sun tabbatar da kuɓutar da mutanen a wata sanarwa da suka fitar a ranar Litinin a birnin Lokoja ta bakin mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, Afusat Saliu Oyiza.
A farkon makon da ya gabata ne a ka yi garkuwa da yan bautar ƙasar lokacin da su ke tafiya akan titin Aloma-Egane cikin wata motar bas a karamar hukumar Ofu ta jihar.
Yan NYSC din na kan hanyarsu ne ta dawowa daga sansanin horar da masu yiwa ƙasa hidima dake ƙaramar Kolokuma/Opokuma ta jihar Bayelsa lokacin da aka kai musu farmaki.
Tun farkon faruwar lamarin rundunar ta samu nasarar ceto mutane 10 daga cikin waɗanda aka yi garkuwar da su a ciki har da direbobin motoci biyun da yan bindigar suka tare.