Hakeem Baba-Ahmad ya ce dole jam’iyun adawa su haɗe kai kafin su iya kayar da Tinubu

Hakeem Baba-Ahmad, shugaban jam’iyar PRP na ƙasa ya ce dole ne jam’iyun adawa su haɗe kansu su kawar  da shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu daga kan mulki a zaɓen shekarar 2027.

Baba-Ahmad ya faɗi haka ne a ranar Litinin a wurin taro jam’iyun adawa na Najeriya da kungiyar G100 ta shirya a Abuja.

Ya ce kawar da shugaban ƙasa Tinubu daga mulki abu ne da ya zama wajibi kuma dole hakan ya tabbata da taimakon ƴan Najeriya.

“Amma kuma yiyuwar faruwar haka zai samu tagomashi ne idan mun yadda munyi aiki tare” ya ce.

” Ba wata jam’iyya da za ta fito fili ta iya cewa ita kaɗai za ta iya kayar da jam’iyyar APC. Babu wata jam’iyya a cikin shida da suke nan wurin da  ba ta fuskantar barazanar da za ta iya rusa ta. babu.”

“dukan mu muna da ƙara a gaban kotu. akwai kokarin da ake na  ganin an durkusar damu, an rusa mu amma baza mu rusu ba saboda muna wakiltar yan Najeriya ne. An kai mu bango an ma zamu mayar da martani.”

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...