Tinubu zai lashe zaɓen 2027 da kaso 65 na kuri’un da za aka kaɗa – Abdulmumin Jibrin

Sulaiman SaadArewaHausa29 minutes ago



Abdulmumin Jibrin, ɗan majalisar  wakilai ta tarayya daga jihar Kano da ke wakiltar mazabar Kiru/Bebeji ya ce Shugaba Bola Tinubu zai samu kashi 65 cikin ɗari na ƙuri’un da za a kada a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Jibrin ya yi wannan magana ne a shirin ‘Politics Today’ na gidan Talabijin na Channels  a ranar Laraba, inda ya tattauna batutuwan da suka shafi tazarcen shugaban ƙasa da kuma rikicin da ke tsakanin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da Nyesom Wike, ministan Babban Birnin Tarayya (FCT).

Tinubu ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2023 a ka ƙarƙashin APC, inda ya doke Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban ƙasa da ya yi takara a  jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), da kuma Peter Obi na jam’iyyar Labour Party.

Shugaban ƙasa na neman a sake zaɓen sa shugabanci karo na biyu kan ƙarkashin APC, inda Atiku da Obi suma ke cikin manyan ‘yan takara.

Sai dai Jibrin ya ce yanayin siyasar Najeriya ya sauya sosai tun bayan zaɓen da ya gabata, lokacin da Tinubu ya samu ƙuri’u 8,794,726, wanda ya kai kashi 36.61 cikin ɗari na sahihan ƙuri’u  da aka kada.

Ya ce: “Mutane suna magana kan ƙarfin sauran jam’iyyun adawa da shugabanninsu, amma abin da suka kasa fahimta shi ne cewa 2023 ba 2027 ba ne. Ina gaya muku yau: shugaban ƙasa ba zai samu ƙasa da kashi 65 cikin ɗari na ƙuri’un da za a kaɗa ba.”

Jibrin ya ce APC ta yi nazari kan shugabannin adawa da motsinsu kafin zaɓen.

“Mun san su sosai kuma muna da tsari na musamman,” in ji shi. “Ina ba ku tabbacin kashi 100 cewa muna gaba sosai da su. Za mu lashe zaɓen.”

Ya kuma bayyana cewa sakamakon zaɓen, ba wai hasashen ra’ayi ba, zai fi bayyana yanayin siyasar ƙasar.

Jibrin ya ce yana sa ran shugaban ƙasa zai yi fice a arewa, duba da ƙoƙarin da ake yi na gyara wasu mummunan fahimta da aka yi game da shi a yankin.

“Eh, akwai ƙalubale. Duk wanda ya ce babu ƙalubale kamar wanda ya ce shugaban ƙasa bai sha baƙar magana ba a arewa. Wannan karya ce,” in ji shi. “Amma muna gyara waɗannan abubuwa. Zan gaya muku abu ɗaya: shugaban ƙasa bai taɓa samun ƙauna kamar yadda yake samu a yanzu a arewa ba.”

Jibrin ya kuma kare Wike a rikicinsa da gwamnonin APC, inda ya bayyana ministan FCT a matsayin “ɗan siyasa mai amfani” ga jam’iyyar.

“Wike mai gyara ne, kuma kana buƙatar mai gyara, kuma duk wanda ya ƙaunaci shugaban ƙasa kuma yake son mu lashe zaɓen nan,” in ji shi. “Ba na cewa Wike Allah ne, amma wannan ba lokacin da za a raina shi ko a yi fada da shi ba.”

Ya ce gwamnonin jam’iyyar za su iya sarrafa Wike saboda duk da halayensa na musamman, yana da ƙima ga jam’iyyar.

Wike, wanda ɗan jam’iyyar PDP ne da Tinubu ya naɗa minista a 2023, yana jagorantar “Rainbow Coalition”, wata haɗin gwiwar jam’iyyu da ke goyon bayan tazarcen Tinubu a 2027.

A ranar Litinin, kungiyar Progressive Governors Forum (PGF), wacce ta haɗa gwamnonin APC, ta ce ba za ta goyi bayan kowace yarjejeniya ta siyasa da za ta raunana jam’iyyar ba.

Sai dai a ranar Alhamis, Wike ya mayar da martani, inda ya bayyana gwamnonin APC a matsayin “marasa kuzari a siyasa”, yana mai cewa Tinubu ya san da “Rainbow Coalition” da duk ayyukansa na siyasa kafin zaɓen 2027.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...