

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya ce daga cikin gwamnonin arewa 19, guda shida ne kawai suka goyi bayan takarar shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu a zaɓen 2023.
Shettima ya yi wannan magana ne a fadar Sarkin Ilorin, Mai Martaba Ibrahim Sulu-Gambari, yayin bikin nadin gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, a matsayin Sardaunan Ilorin.
Ya ce Tinubu ya fuskanci mawuyacin yanayi a siyasa amma bai yi kasa a gwiwa ba wajen cimma burinsa.
“Kun san muna da jihohi 19 a arewa. Daga cikin waɗannan, guda shida ne kawai suka gaskata kuma suka goyi bayan Tinubu,” in ji Shettima.
Ya ambaci tsohon gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello, da gwamnan Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, sannan ya ce ba zai ci gaba da kiran sunayen sauran ba don kauce wa cece-kuce.
Shettima ya bayyana cewa duk da ƙalubalen da Tinubu ya fuskanta, ya ci gaba da tafiya har ya cimma nasara.
Ya ƙara da cewa wannan darasi ne ga ‘yan siyasa cewa sabani a zaɓe bai kamata ya raba su har abada ba.
Bayan zaɓen 2023, Shettima ya ce Tinubu ya runguma tare yafe wa duk sauran gwamnonin arewa da ba su goyi bayan sa ba, yana mai kiran hakan alamar jagora nagari.
Ya yi kira ga ‘yan siyasa da masu rike da mukaman gwamnati su yi aiki da tawali’u, yana mai jaddada cewa mulki na wucin gadi ne kuma Allah ne ke ba wa wanda Ya so.
Shettima ya kuma kare salon gwamnatin Tinubu wajen tafiyar da tattalin arziki, yana mai cewa gwamnatin ta fi son tinkarar matsalolin da ta gada maimakon ta dinga zargin shugabannin baya.
Ya bayyana cewa gwamnatin ta gaji kusan dala biliyan 3.9 a asusun gwamnati, tare da matsalolin tattalin arziki masu tsanani. Duk da haka, Tinubu ya ci gaba da aiwatar da sauye-sauye.
Shettima ya ce salon siyasar Tinubu ya yi kama da na tsohon shugaban ƙasa marigayi Muhammadu Buhari, wanda ya kasance ba ya yarda a matsa masa lamba a tattaunawar siyasa.
Bikin nadin ya samu halartar gwamnonin jihohi, shugabannin siyasa, sarakunan gargajiya da sauran manyan bakii