Dangote ya faɗi dalilin da ya saka man fetur ya ke tsada a Najeriya



Kasuwar man fetur ta Najeriya na iya fuskantar babbar matsalar samuwar man fetur fiye da farashi sakamakon rikice-rikicen siyasa a duniya da ke girgiza kasuwar makamashi.

Wannan gargadin ya fito ne daga Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Aliko Dangote. 

Dangote ya ce rikicin da ake yi a Gabas ta Tsakiya na iya jawo matsin lamba ga hanyoyin da ake  bi wajen. samar da man fetur, inda hakan zai iya karkatar da hankali daga farashin da direbobi ke biya zuwa ɗasa ayar tambayar ko za a iya samun isasshen man fetur. 

Ya ce: “Matsalar yanzu, gaba, dole in gargadi cewa wannan rikicin a Gabas ta Tsakiya ba batun farashi ba ne; batun samun man ne baki ɗaya.” 

Wannan gargadi ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan tsadar man fetur a Najeriya. 

Masu amfani da man fetur suna fama da tsadar sufuri da rayuwa bayan tashin farashin man fetur tun bayan cire tallafin mai. 

Sai dai Dangote ya jaddada cewa kasuwar Najeriya ya kamata a duba ta bisa ga abin da ke faruwa a ƙasashen makwabta. 

Ya ce ana sayar da man fetur a can da tsada sosai, wanda ke haifar da bambancin farashi da ke ƙarfafa safarar man Najeriya zuwa ƙasashen waje. 

Ya ce: “Ban san ko ka sani ba, har yanzu ana safarar man fetur da muke samarwa zuwa ƙasashen makwabta.” 

Dangote ya bayyana bambancin farashin tsakanin Najeriya da wasu ƙasashen makwabta a tsakanin kashi 30 zuwa 50 cikin ɗari. 

Ya ce irin wannan bambanci yana sa safarar haramtacciya ta zama abin jan hankali. 

Ya kawo misali da Jamhuriyar Nijar, inda man fetur zai iya yin tsada da kashi 20 zuwa 25 cikin ɗari fiye da Najeriya. 

Ya yi amfani da farashin Naira 1,350 a kowace lita a Najeriya a matsayin misali, yana tambaya ko akwai wata kasuwanci da za ta iya ba ‘yan kasuwa riba ta kashi 25 cikin ɗari nan take. 

Ya ce: “Wane irin kasuwanci za ka yi da zai ba ka riba ta kashi 25 cikin ɗari nan take?” 

Dangote ya ce wannan riba na iya ƙarfafa gwiwar masu karkatar da man fetur da aka tanada wa ‘yan Najeriya zuwa iyakokin ƙasa, inda ake sayar da shi da tsada. 

Ya ce: “Kana nuna kamar kana kai shi Sokoto, sai ka karkata ka kai Ilela, ka sayar.” 

Duk da yiwuwar matsalar samuwa, Dangote ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa matatar man sa za ta ci gaba da samar da man fetur ga kasuwar cikin gida. 

Ya ce: “Za mu samar wa Najeriya. ‘Yan Najeriya ba su da abin da za su damu da shi. Ba za a samu karanci daga bangarenmu ba. Ba za a samu karanci ba. Ba za a samu layi ba. Za mu tabbatar da cewa muna gamsar da kasuwa duk da dukkan ƙalubale.” 

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...