Mutane arewa basu da dalilin ƙin zaɓar Tinubu a karo na biyu – Yari

Sulaiman SaadHausaArewa29 minutes ago


Daraktan Janar na Kwamitin Yaƙin Neman Zaben Shugaban Ƙasa na jam’iyyar APC  Abdulaziz Yari, ya ce yankin Arewa ba shi da wani dalili da zai hana shi goyon bayan neman wa’adin mulki karo  na biyu da Shugaba Bola Tinubu zai yi a  zaben 2027.

Yari ya yi wannan magana ne  a Legas lokacin da ya jagoranci mambobin PCC zuwa fadar Rilwan Akiolu, Sarkin Legas, a wani bangare na shirye-shiryen kwamitin kafin zaben 2027.

Tsohon gwamnan jihar ta Zamfara ya ce ya kamata Arewa ta saka wa Tinubu saboda irin goyon bayan da ya bai wa tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a lokacin da ya tsaya takara da kuma lokacin da aka sake zabensa.

A cewar Yari, Tinubu ya ki amincewa da matsin lamba da aka yi masa na ya tsaya takara a zaben 2019 da Buhari, inda ya nace cewa lokaci ne na Arewa ta samar da shugaban ƙasa.

Yari ya ce: “A gare mu ‘yan Arewa, lokaci ya yi da za mu saka wa Tinubu saboda ya bari Arewa ta kammala wa’adinta. Na tuna akwai wani rikici daga wasu masu neman mulki a cikin APC da suka yi ƙoƙarin shawo kan Tinubu ya tsaya takara a 2019. Amma ya ƙi, ya ce lokaci ne na Arewa. Ya ce muddin Buhari zai iya fitowa ya nemi kuri’a, zai tsaya tare da shi har ƙarshe. Kuma hakan ne ya yi.” ya ce.

Yari, wanda yanzu yake wakiltar mazabar Zamfara ta Yamma a Majalisar Dattawa, ya ce goyon bayan da Tinubu ya bai wa Buhari ya zama dalilin da zai sa ‘yan Arewa su saka masa ta hanyar mara masa baya a 2027.

Ya ce ya kamata yankin Arewa ya goyi bayan Tinubu bisa ga abin da ya kira nasarorin da shugaban ya samu da kuma ƙoƙarin gwamnatinsa wajen magance matsalolin da ya gada daga gwamnatoci da suka gabata.

“A yau, ban ga wani uzuri ba daga yankin Arewa da zai hana mu goyi bayan Tinubu ya ci gaba da aikin alherin da ya fara kuma ya kammala wa’adinsa,” a cewar Yari.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...