Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta yi Allah-wadai da harin da wasu ‘yan bindiga suka kai wa al’ummar Irigwe da ke Angwan Magaji a Karamar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane tara tare da jikkata wasu goma sha daya.
Kungiyar ta bayyana cewa harin ya faru ne a daren ranar 16 ga watan Yuni, 2026. Daga cikin wadanda suka mutu akwai yara biyu masu shekaru biyar da hudu.
Amnesty International ta ce har yanzu ana ci gaba da neman wasu mazauna yankin da ba a san inda suke ba bayan harin. Ta kuma bayyana lamarin a matsayin daya daga cikin munanan hare-haren baya-bayan nan da suka afku a Kudancin Kaduna.
A cewar kungiyar, hare-haren kashe-kashe, garkuwa da mutane da sauran ayyukan ta’addanci na ci gaba da barazana ga al’ummomin yankin.
Kungiyar ta bukaci hukumomi su dauki matakan gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyi tare da tabbatar da hukunta wadanda ke da hannu a irin wadannan hare-hare. Ta kuma gargadi cewa rashin gurfanar da masu laifi a gaban kuliya na kara jefa rayuwar mazauna yankin cikin hadari.
Amnesty International Ta Yi Allah-Wadai Da Harin Da Ya Kashe Mutane Tara A Kaduna

