Dakarun Najeriya Sun Lalata Maboyar Da Ake Zargin ‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Ita A Neja



Dakarun FOB AUDU da FOB BABANNA sun lalata wata maboyar da ake zargin ‘yan ta’adda na amfani da ita a yankin Borgu da ke Jihar Neja.

Rahoton da masanin harkokin tsaro Zagazola Makama ya wallafa ya ce dakarun sun kai samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri kan wani sansanin da ake zargin na ‘yan ta’adda ne a yankin Saminaka–Kanau.

Ko da yake ba a yi arangama da wadanda ake zargin ba yayin aikin, dakarun sun gano tare da rusa maboyar. Haka kuma sun lalata wani wuri da ake zargin ana amfani da shi wajen adana kayayyaki da gudanar da harkokin kungiyar.

Majiyoyin soja sun tabbatar da cewa an gudanar da aikin cikin nasara ba tare da wata matsala ba.

Rahoton ya kara da cewa jami’an tsaro na ci gaba da mamaye yankin domin hana miyagu samun damar gudanar da ayyukansu.

More from this stream

Recomended