INEC Ta Dawo Da Shugabancin Mark A ADC A Shafinta Na Yanar Gizo Bayan Hukuncin Kotun Koli




Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta sabunta shafinta na intanet inda ta saka David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC da Rauf Aregbesola a matsayin sakatare.

An ga wannan sauyi ne a ranar Alhamis da yamma, bayan hukuncin kotun koli kan rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar.

A baya, INEC ta cire shugabancin bangaren Mark daga shafinta bisa hukuncin kotun daukaka kara. Sai dai bangaren Mark da kuma Nafiu Bala duk sun kasance suna ikirarin shugabancin jam’iyyar.

Kotun koli ta umarci Mark ya koma babbar kotun tarayya domin ci gaba da sauraron shari’ar rikicin shugabancin.

Har ila yau, kotun kolin ta soki umarnin kotun daukaka kara da ya bukaci a ci gaba da kasancewa a yadda al’amura suke kafin fara shari’a.

Bayan wannan hukunci, INEC ta sake dawo da cikakken jerin shugabannin jam’iyyar ADC a shafinta, karkashin jagorancin David Mark.

More from this stream

Recomended