
An rantsar da Dr Peter Akpe a matsayin mataimakin gwamnan jihar Bayelsa inda zai karasa shekaru biyu da su ka rage na wa’adin gwamnatin jihar.
Majalisar dokokin jihar ce ta tantance tare da tabbatar da Akpe a matsayin mataimakin gwamnan jihar bayan da gwamnan jihar Douye Diri ya mika sunansa domin maye gurbin marigayi tsohon mataimakin gwamnan da ya mutu.
Kafin ya zama mataimakin gwamnan Akpe shi ne ke rike da mukamin shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar.
Babbar alkaliyar jihar Bayelsa, mai shari’a Matilda Abrakasa Ayemieye ce ita ce ta rantsar da sabon mataimakin a wani biki da aka gudanar a dakin taron majalisar zartarwa na gidan gwamnatin jihar dake Yenagoa.
A yayin taron an kuma rantsar da kwamishina guda É—aya da kuma manyan sakatarorin dindindin guda 18.
Akpe ya maye gurbin, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo tsohon mataimakin gwamnan da ya mutu a ranar 11 ga watan Disambar shekarar 2025.

