Wata Likita Ta Riga Mu Gidan Gaskiya Bayan Ta Haifi ‘Yan Uku

Wata likita mai suna Ere Siana Sintei Ogbachi ta rasu sakamakon wasu matsaloli bayan ta haifi ‘yan uku a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Niger Delta (NDUTH) da ke Okolobiri, a jihar Bayelsa.

Iyalinta sun ce bayan nasarar haihuwar, likitar ta fara samun sauƙi daga jinya, sai dai daga bisani lafiyarta ta tsananta kwatsam.

Daga nan ne aka mayar da ita sashen kula da marasa lafiya masu tsananin bukatar kulawa (ICU) na Asibitin Tarayya da ke Yenagoa domin ci gaba da jinya.

Duk da ƙoƙarin likitoci na ceton rayuwarta, an tabbatar da rasuwarta a safiyar ranar 14 ga watan Afrilu, 2026.

A wata sanarwa da wani dan uwanta Meshack N. Sintei ya fitar, iyalan sun bayyana rasuwarta a matsayin babban rashi, inda suka ce duk matakan da aka dauka domin ceton ta ba su yi nasara ba.

Marigayiyar likita an bayyana ta a matsayin kwararriyar ma’aikaciyar lafiya, uwa kuma mai ‘ya’ya uku da ta bari, tare da kasancewarta mamba a ƙungiyar likitocin Najeriya.

More from this stream

Recomended