
Shugaban kasa Bola Ahmad zai kai ziyarar aiki ta kwana guda jihar Kebbi a ranar Asabar.
A wata sanarwa ranar Juma’a mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya bayyana cewa a yayin ziyarar Tinubu zai kaddamar da wasu ayyuka da gwamnan jihar Nasir Idris ya aiwatar.
Onanuga ya ce shugaban kasar zai kuma kasance baƙo na musamman a wurin bikin kamun kifi na Argungu karo na 61.
Ya kara da cewa bikin kamun kifin na daga cikin bukukuwan al’adu da suka shahara a Nahiyar Afirka inda ake yinsa gefen kogin Matan Fada.

