Tinubu zai kai ziyara jihar Kebbi ranar Asabar

Shugaban kasa Bola Ahmad zai kai ziyarar aiki ta kwana guda jihar Kebbi a ranar Asabar.

A wata sanarwa ranar Juma’a mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya bayyana cewa a yayin ziyarar Tinubu zai kaddamar da wasu ayyuka da gwamnan jihar Nasir Idris ya aiwatar.

Onanuga ya ce shugaban kasar zai kuma kasance baƙo na musamman a wurin  bikin kamun kifi na Argungu karo na 61.

Ya kara da cewa bikin kamun kifin na daga cikin bukukuwan al’adu da suka shahara a Nahiyar Afirka inda ake yinsa gefen kogin Matan Fada.

More from this stream

Recomended