
Peter Obi tsohon ɗan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyar LP ya sake bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara a zaben shekarar 2027.
Obi ya fadi haka ne a lokacin da ya halarci taron yakin neman zaben ɗantakar jam’iyar ADC a zaɓen karamar hukumar AMAC dake birnin tarayya Abuja.
” Kunga wannan zaben mai zuwa, ku goyi bayan mu a AMAC zai taimake ni sosai. Goyon bayanku a AMAC na da matukar muhimmanci a tafiyar siyasar mu na tsunduma ciki kuma zan yi takarar shugaban kasa. Idan na dawo za ku ga ni,” ya ce.
Tun bayan da ya shiga jam’iyar APC magoya bayan Obi ke shawartar jam’iyar ta tsayar da shi a matsayin ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen 2027.

