
Gwamnatin jihar Niger ta ce mutane sama da 700 ne suka yi batan dabo biyo bayan ambaliyar ruwa da aka yi a garin Mokwa hedkwatar karamar hukumar Mokwa ta jihar.
Gwamna Umar Bago na jihar shi ne ya bayyana haka lokacin da yake karbar bakuncin, Manjo Hamza Al-Mustapha tsohon dogarin janar Sani Abacha da shi da abokanansa a yayin da suka kai ziyarar ta’aziya da jaje a Minna ranar Talata kan ambaliyar ruwan.
Bago wanda ya samu wakilcin mataimakin gwamnan jihar, Yakubu Garba ya bayyana cewa mutane 207 ne aka tabbatar sun mutu a yayin da wasu 3000 suka rasa muhallinsu.
“Sama da mutane 700 ne suka bace har kawo yanzu mun gaza gano inda su ke. Ambaliyar tayi barna sosai,” ya ce .
Ya kara da cewa ambaliyar ruwan ta lalata gidaje 400 a yayin da ta ruguza gidaje 283 da shaguna 50.
Bago ya ce gwamnatin jihar na aiki da kungoyin kwararru domin lalubo musabbabin ambaliyar.
Tun da farko Al-Mustapha ya ce sun kawo ziyarar ne domin jajantawa gwamnatin jihar Niger da kuma al’ummar Mokwa biyo bayan mummunan ambaliyar.