
Dakarun rundunar Operation Hadin Kai A wani tsararren farmaki na hadin gwiwa tsakanin sojan ruwa na sama da kuma na kasa sun kashe mayakan Boko Haram/ISWAP da dama bayan da su ka yi yunkurin kai farmaki kan wani sansanin sojan ruwan Najeriya dake yankin tafkin Chadi a ranar da tsakar daren ranar Laraba.
Yan ta’addar dauke da makamai sun kaddamar da farmaki kan sansanin sojan ne da karfe biyu na dare a kokarinsu na lalata wasu jiragen ruwa na gyara hanyar ruwa mai sarkakiya da gwamnatin jihar Borno ta samar.
Maharan sun fuskanci turjiya daga dakarun dake sansanin da kuma dauki da suka samu daga sojojin dake Baga a wata musayar wuta da aka dauki sama da sa’o’i biyu ana yi.
Yan ta’adda da dama aka kashe a yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga a yayin da sojan sama suka cigaba da bin sawunsu da ruwan wuta.
Har ila yau dakarun sun gano wasu nakiyoyi biyu da sauran kayayyaki na ta’addar.maya