Wasu ƴan bindiga sun kashe wani mai sana’ar POS a garin Ado-Ekiti babban birnin jihar Ekiti.
Mai sana’ar ta POS dake da suna Alfa Taofeek an harbe shi ne a shagonsa dake wajen Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Ekiti.
Majiyoyi da dama sun bayyana cewa ƴan bindigar sun isa shagon marigayin akan babur inda suka buɗe masa wuta suka tsere da kuɗaɗen da ba a san adadin su ba.
Taofeek ƙaramin fitaccen ɗan kasuwa ne abin da ya sa ko da yaushe akwai kuɗaɗe a hannunsa saboda yanayin kasuwancinsa.
Babu jimawa kaɗan ƴan bindigar sun sake harbe wani mutum mai sayar da shinkafa a kasuwar Bisi dake Ado-Ekiti.
Abun da ya tilastawa ƴan kasuwa da masu sayayya tserewa da ƙafafunsu.
Abutu Sunday mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Ekiti ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce kawo yanzu ba a kama waɗanda suka aikata kisan ba sai dai tuni rundunar ta baza komarta.