Gwamnatin Zamfara ta umarci jami’an tsaro su harbe masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya umarci jami’an tsaro da su dauki tsattsauran mataki kan mutanen da suke aikin haƙar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar.

A wata sanarwa ranar Asabar, mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Idris ya ce tsawon shekaru hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba na ruruta wutar rikicin yan bindiga da kuma sauran ayyukan laifi a jihar.

A cewar mai magana da yawun gwamnan ya ce lokaci ya yi da za a kawo karshen ayyukan haƙar ma’adanan tare da aiwatar da matakan da za su kare lafiyar al’umma.

A saboda haka aka umarci jami’an tsaro da su yi ta maza su harbe duk wanda aka samu da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

“Umarnin ya zama dole domin kare lafiya da tsaron al’ummar jihar Zamfara da kuma razana wadanda suke shirin aikata aiki irin haka.” a cewar sanarwar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]