Ɗantakar NNPP a zaɓen gwamnan jihar Ondo ya janye takararsa

Israel Ayeni ɗantakar gwamnan jihar Ondo ƙarƙashin jam’iyar NNPP ya janye daga takarar da yake yi.

A ranar 16 ga watan Nuwamba ne aka shirya gudanar da zaɓen gwamnan jihar.

26 ga da watan Afrilu ita ce ranar da aka gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyar ta NNPP inda Ayeni ya kayar da abokin karawarsa a zaɓen Ibrahim Ajagunna da  kuri’a 100.

A wasikar yanje takarar ta sa da aka fitar ranar Laraba a Akure babban birnin jihar, ɗantakar ya ce matakin da ya ɗauka shi ne zai amfani jam’iyar.

Peter Olagookun shugaban jam’iyar NNPP na jihar Ondo ya ce Ayeni ya janye takarar ne a ƙashin kansa domin jam’iyar ta samu damar tsayar da ɗantakara nagartacce.

Olagookun ya ce za a gudanar da zaɓen fitar da gwani na maye gurbin ɗantakar a ranar Laraba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]