Jam’iyar APC ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin jihar Edo

Jam’iyar APC ta lashe zaɓen dukkanin kujerun shugabannin ƙananan hukumomi 18 da kansiloli 192 da aka gudanar a jihar Edo.

Da yake sanar da sakamakon zaɓen ranar Lahadi, shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Edo, Jonathan Aifuobhokhan ya ce jam’iyar ta yi nasara a dukkanin kananan hukumomin da kuma mazabun jihar da aka gudanar da zaɓe.

Aifuobhokhan wanda ya gaza bayyana kuri’un  da jam’iyar ta samu a kowace karamar hukuma ya ce an gudanar da zaɓen  lami lafiya a dukkanin ƙananan hukumomin da kuma mazaɓun.

Ya ce an tantance masu kaɗa kuri’a, kaɗa kuri’a,ware kuri’a, kirgawa da kuma sanar da sakamako kamar yadda dokar zaɓen ƙananan hukumomi ta jihar Edo ta shekarar 2022 ta tanada.

Shugaban hukumar zaɓen ya bayyana gamsuwar da irin ƙoƙarin da jami’an ayyana sakamakon zaɓen kan kwarewar da suka

More from this stream

Recomended