
Yan bindiga sun yi garkuwa da wani shugaban wata makarantar firamare ta makiyaya dake Igbojaye a karamar hukumar Itesiwaju ta jihar Oyo inda suka bukaci a biya su miliyan 30 a matsayin kuɗin fansa.
Shugaban makarantar mai suna Matthew Owoade mai shekaru 60 sanannen mutum ne a yankin an yi garkuwa da shi da maraicen ranar Asabar da misalin karfe 05:00 zuwa 06:00.
Lamarin na zuwa ne kasa da sa’o’i 24 bayan da jami’an tsaro suka ceto dalibai da malamai da wasu yan bindiga su ka yi garkuwa da su a karamar hukumar Oriire ta jihar bayan da su ka shafe kwanaki 56 a hannun masu garkuwar.
Dan gidan shugaban makarantar firamaren, Abiola Owoade ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce ya faru ne lokacin da mahaifinsa ke dawowa daga gonarsa dake Budo Aare a cikin ƙaramar hukumar ta Itesiwaju.
” Ba a jima ba kaɗan da yin garkuwar masu garkuwar su ka tuntubi iyalan ta hanyar yin amfani da wayar sa inda su ka bukaci a biya su miliyan 30 kafin a sake shi ” ya ce.
” Amma kuma da misalin karfe 08:20 na safiyar ranar Lahadi 12 ga watan Yuli aka gano babur dinsa a aka yar a cikin daji bayan da aka gudanar da bincike,”
Dan shugaban makarantar ya roki hukumomin tsaro da su taimaka su kuɓutar da mahaifin nasa.

