Rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta kama mutane 15 bayan wani rikici tsakanin wasu kungiyoyin matasa a garin Azare da ya jikkata akalla mutum 10.
Mai magana da yawun rundunar, SP Nafiu Habib, ya ce lamarin ya faru ne tsakanin matasan unguwannin Tsakuwa da Matsango, inda jami’an ’yan sanda suka isa wurin cikin gaggawa suka tarwatsa masu rikicin.
An kai wadanda suka jikkata Asibitin Koyarwa na Jami’ar Tarayya ta Kimiyyar Lafiya da ke Azare domin samun kulawa.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya kai ziyara yankin da abin ya shafa da kuma asibitin da aka kwantar da wadanda suka jikkata.
Ya umarci a ci gaba da sintiri na sa’o’i 24 tare da zurfafa bincike domin gano musabbabin rikicin da kuma kamo sauran wadanda suka tsere, yana mai gargadin cewa duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci.
Ƴansanda Sun Kama Mutum 15 Bayan Rikicin Matasa a Azare

