Ƴanbindiga Sun Sace Matafiya 28 a Jihar Filato

Rahotanni sun nuna cewa wasu ƴanbindiga sun yi awon gaba da matafiya 28 daga garin Zak da ke yankin Bashar a ƙaramar hukumar Wase ta jihar Filato.

Wani mazaunin ƙaramar hukumar ya tabbatar wa jaridar Daily Trust faruwar lamarin, inda ya ce mutanen da aka sace—maza da mata da yara—na kan hanyarsu ta zuwa garin Sabon Layi ne domin halartar taron Maulidi a ranar Lahadi.

Wani mazaunin garin ya kuma bayyana cewa zuwa yanzu babu wani bayani kan inda mutanen da aka sace suke.

A halin da ake ciki, mai magana da yawun ƴansandan ƙasar, SP Alabo Alfred, ya ce rundunar tana bincike kan rahoton faruwar lamarin.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]