Ƴanbindiga Sun Sace Matafiya 28 a Jihar Filato

Rahotanni sun nuna cewa wasu ƴanbindiga sun yi awon gaba da matafiya 28 daga garin Zak da ke yankin Bashar a ƙaramar hukumar Wase ta jihar Filato.

Wani mazaunin ƙaramar hukumar ya tabbatar wa jaridar Daily Trust faruwar lamarin, inda ya ce mutanen da aka sace—maza da mata da yara—na kan hanyarsu ta zuwa garin Sabon Layi ne domin halartar taron Maulidi a ranar Lahadi.

Wani mazaunin garin ya kuma bayyana cewa zuwa yanzu babu wani bayani kan inda mutanen da aka sace suke.

A halin da ake ciki, mai magana da yawun ƴansandan ƙasar, SP Alabo Alfred, ya ce rundunar tana bincike kan rahoton faruwar lamarin.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]