‘Yan bindiga Sun Kashe Fulani Makiyaya Bakwai A Filato

VOA Hausa
Wasu ‘yan bindiga sun hallaka makiyaya bakwai a kauyen Dogon-Gaba dake karamar hukumar Jos ta Kudu a jihar Filato a tsakiyar arewacin Najeriya.
Mahaifin daya daga cikin wadanda aka kashen, Ibrahim Makaho ya ce maharan sun fito ne ta yankin Kwall a karamar hukumar Bassa, a wata mota kirar J5.
“Kamar wadanda suka gani suka shaida mana, sun z da J5 suka tsaya a daidai wnai kauye Danda, yaranmu suna kiwo a wurin ba san komai ba, suka biyo su har wani kauye da ake cewa dogon gaba, anan suka kashe yara guda bakwai, aka kashe shanu aka tura wasu aka tafi da su.” In ji Ibrahim Makaho.
Kai wa juna hari da ramakon gayya tsakanin Fulani makiyaya da manoma a kananan hukumomin arewacin jihar Filato ya kasance barazana ga zaman lafiya a yankin.
Kakakin kungiyar kabilar Irigwe, wadanda makiyayan ke dora alhakin kisan akansu, Davidson Malison ya ce ba su da labari kisan.
“Gaskiya yanzu nake ji daga wurinki…. gakisya ban san da wani abu haka ba, kuma ina ganin mutanenmu ba su yi wani abu haka ba.” In ji Malison.
Shugaban kungiyar hadaddiyar kungiyoyin matasan Fulani a Najeriya, Abdulkarim Bayero yayi kiran da akai zuciya nesa.
Kwamishinan yada labarai da sadarwa a jihar Filato, Mr. Dan Manjang ya ce a kwanannan gwamnati ta sayo motoci da sauran na’urorin tsaro ta kuma horadda matasa dubu uku a dukkan kananan hukumomin jihar wadanda za su taimaka wa jami’an tsaro da bayanai.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...