Ƴan ta’adda sun kai hari wasu bankuna a Benue

Wasu ‘yan bindiga ɗauke da makamai sun kashe mazauna garin Otukpo da ke jihar Benue da ba a tantance adadinsu ba.

Rahotanni sun nuna cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki wasu bankuna a Otukpo da misalin karfe 3 na yammacin ranar Juma’a, inda suka rika harbe-harbe.

Wani ganau Sunday Abah da ya ce ‘yan bindigar sun shafe sa’o’i da dama suna gudanar da ayyukansu ba tare da jami’an tsaro sun kawo agaji ba.

“’Yan fashi da makami sun mamaye ko’ina a Otukpo. Suna harbin wanda suka gani kawai. “A halin yanzu, suna fashi a bankin Zenith kuma sun shafe sama da awanni uku suna nan,” in ji shi.

Ba a samu damar tuntubar jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sandan jihar Benue, DSP Catherine Anene Sewuese ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...