Ƴan ta’adda sun kai hari wasu bankuna a Benue

Wasu ‘yan bindiga ɗauke da makamai sun kashe mazauna garin Otukpo da ke jihar Benue da ba a tantance adadinsu ba.

Rahotanni sun nuna cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki wasu bankuna a Otukpo da misalin karfe 3 na yammacin ranar Juma’a, inda suka rika harbe-harbe.

Wani ganau Sunday Abah da ya ce ‘yan bindigar sun shafe sa’o’i da dama suna gudanar da ayyukansu ba tare da jami’an tsaro sun kawo agaji ba.

“’Yan fashi da makami sun mamaye ko’ina a Otukpo. Suna harbin wanda suka gani kawai. “A halin yanzu, suna fashi a bankin Zenith kuma sun shafe sama da awanni uku suna nan,” in ji shi.

Ba a samu damar tuntubar jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sandan jihar Benue, DSP Catherine Anene Sewuese ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]