Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai akan hanyarsu ta zuwa rubuta jarabawar UTME

Wasu da ake zargin yan bindiga ne dauke da makamai sun yi garkuwa da wasu ɗalibai akan  hanyarsu ta zuwa wurin rubuta jarabawar shiga  jami’a ta UTME.

Lamarin ya faru ne akan titin Makurdi zuwa Otukpo a jihar Benue.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Benue, Anene Sewuse ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis amma ba tare da bayar da cikkaken bayani ba.

“Ka ce kana son ka tabbatar. Tabbas ya faru,” a cewarAnene a lokacin da take zantawa da wakilin jaridar The Cable.

Daliban da aka sace na daga cikin fasinjojin dake tafiya a cikin wata motar haya ranar Laraba da daddare.

A cewar rahotanni da dama yawancin waɗanda aka garkuwar da su ɗalibai  yan mata da kuma maza matasa dake kan hanyarsu ta zuwa cibiyoyin da za su rubuta jarabawar.

Jaridar Punch ta rawaito cewa daya daga cikin fasinjojin da kuma direban motar sun samu nasarar tserewa jaridar ta kuma kara da cewa kwamishinan yan sandan jihar, Ifeanyi Emenari ya bayyana cewa fasinjoji 14 aka yi garkuwa da su.

More from this stream

Recomended