Ƴan Sanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Ƴan sanda a jihar Adamawa sun kama wani mutum, Aminu Abubakar ɗan shekara 56 da ya kashe matarsa.

Abubakar mazaunin unguwar Lelewaji a rukunin gidaje na Shagari Phase 2 dake Yola a karamar hukumar Yola South ana zargin sa da dukan matarsa har ta kai ga ta mutu bayan da ya samu labarin ta na shirin yin aure.

Ana zargin cewa Abubakar ya saki matar tasa saki biyu amma kuma ya bata wurin zama har sai ta kammala idda.

Amma kafin ta kammala sai ya samu labarin cewa ta na shirin auren wani mijin na daban abin da ya harzuƙa shi har ta kai ga dukan da ya yi ajalinta.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Adamawa ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar.

More News

Kotu Ta Hana PDP Cire Shugaban Riƙon Jam’iyar

Wata Babbar Kotun Tarayya dake Abuja ta hana jam'iyar PDP dakatar da Umar Damagum daga matsayinsa na shugaban riƙon jam'iyar. Mai Shari'a  Peter Lifu shi...

Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Ziyarar Aiki Da Ya Kai  Saudiya da Nezaland

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasashen Saudiya da Nezaland. A ranar 22 ga watan Afrilu ne...

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...