Ƴan Sanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa

Ƴan sanda a jihar Adamawa sun kama wani mutum, Aminu Abubakar ɗan shekara 56 da ya kashe matarsa.

Abubakar mazaunin unguwar Lelewaji a rukunin gidaje na Shagari Phase 2 dake Yola a karamar hukumar Yola South ana zargin sa da dukan matarsa har ta kai ga ta mutu bayan da ya samu labarin ta na shirin yin aure.

Ana zargin cewa Abubakar ya saki matar tasa saki biyu amma kuma ya bata wurin zama har sai ta kammala idda.

Amma kafin ta kammala sai ya samu labarin cewa ta na shirin auren wani mijin na daban abin da ya harzuƙa shi har ta kai ga dukan da ya yi ajalinta.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Adamawa ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]