Ƴan Sanda Sun Daƙile Wani Harin Ƴan Bindiga A Katsina

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina ta ce ta tarwatsa wani yunkurin harin ’yan bindiga a hanyar Kandawa zuwa Dankar da ke Karamar Hukumar Batsari, inda ta kwato bindigogin AK-47 guda biyu, harsasai 24 da babur.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Abubakar Sadiq, ya bayyana hakan a ranar Asabar. Ya ce wannan abin ya biyo bayan bayanan sirri da suka nuna cewa miyagun mutanen sun shirya tare hanyar domin kai hari.

Sadiq ya ce saurin tashi tsaye da DPO da tawagarsa su ka yi ya sa suka yi arangama da ’yan bindigar, wanda hakan ya tilasta musu tserewa tare da barin makaman da ke hannunsu.

A cewarsa, wannan nasara na cikin sabuwar dabarar da rundunar ta ɗauka tare da bin umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda domin ƙarfafa tsaro a fadin ƙasar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]