Ƴan Sanda Sun Daƙile Wani Harin Ƴan Bindiga A Katsina

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina ta ce ta tarwatsa wani yunkurin harin ’yan bindiga a hanyar Kandawa zuwa Dankar da ke Karamar Hukumar Batsari, inda ta kwato bindigogin AK-47 guda biyu, harsasai 24 da babur.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Abubakar Sadiq, ya bayyana hakan a ranar Asabar. Ya ce wannan abin ya biyo bayan bayanan sirri da suka nuna cewa miyagun mutanen sun shirya tare hanyar domin kai hari.

Sadiq ya ce saurin tashi tsaye da DPO da tawagarsa su ka yi ya sa suka yi arangama da ’yan bindigar, wanda hakan ya tilasta musu tserewa tare da barin makaman da ke hannunsu.

A cewarsa, wannan nasara na cikin sabuwar dabarar da rundunar ta ɗauka tare da bin umarnin Sufeto Janar na ’Yan Sanda domin ƙarfafa tsaro a fadin ƙasar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]