Ƴan sanda sun ceto ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka biyu da aka sace a Anambra

Rundunar yan sandan jihar Anambra ta bayar da sanarwar ceto ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka a Najeriya su biyu da aka yi garkuwa da su a jihar.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Anambra, Ikenga Tochukwu ya ce da tsakar daren ranar Alhamis ne aka samu nasarar ceto mutanen

A ranar Talata ne wasu yan bindiga da ba’asan ko su waye ba suka kai hari kan ayarin motocin ma’aikatan inda suka kashe wasu tare da yin awon gaba da wasu daga cikin ma’aikatan.

Jihar Anambra ta dade tana fama da hare-hare daga yan kungiyar IPOB dake fafutukar kafa kasar Biafra.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]