Rundunar yan sandan jihar Anambra ta bayar da sanarwar ceto ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka a Najeriya su biyu da aka yi garkuwa da su a jihar.
Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Anambra, Ikenga Tochukwu ya ce da tsakar daren ranar Alhamis ne aka samu nasarar ceto mutanen
A ranar Talata ne wasu yan bindiga da ba’asan ko su waye ba suka kai hari kan ayarin motocin ma’aikatan inda suka kashe wasu tare da yin awon gaba da wasu daga cikin ma’aikatan.
Jihar Anambra ta dade tana fama da hare-hare daga yan kungiyar IPOB dake fafutukar kafa kasar Biafra.