Ƴan sanda sun ceto ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka biyu da aka sace a Anambra

Rundunar yan sandan jihar Anambra ta bayar da sanarwar ceto ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka a Najeriya su biyu da aka yi garkuwa da su a jihar.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Anambra, Ikenga Tochukwu ya ce da tsakar daren ranar Alhamis ne aka samu nasarar ceto mutanen

A ranar Talata ne wasu yan bindiga da ba’asan ko su waye ba suka kai hari kan ayarin motocin ma’aikatan inda suka kashe wasu tare da yin awon gaba da wasu daga cikin ma’aikatan.

Jihar Anambra ta dade tana fama da hare-hare daga yan kungiyar IPOB dake fafutukar kafa kasar Biafra.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]