Ƴan fashin daji sun kashe ɗan sanda ɗaya a wani shingen bincike a Zamfara

Ƴan fashin dajin a ranar Lahadi sun kai da farmaki kan wani shingen binciken ƴan sanda inda suka kashe ɗan sanda guda ɗaya tare da jikkata Wasu.

Shingen binciken an kafa shi ne tazarar  ƙasa da kilomita ɗaya kafin ka isa Kwatarkwashi garin dake kusa da Gusau babban birnin jihar.

Majiyoyi da dama sun faɗawa jaridar Daily Trust cewa ƴan fashin dake kan babura sama da 40 sun kai farmakin ne da misalin ƙarfe 04:00 na asubahin ranar Lahadi.

Ƴan fashin sun ƙona duk wani mai muhimmanci da suka samu a shingen binciken kafin su  bar wurin.

A cewar wata majiya ƴan fashin dajin sun samu nasarar fin ƙarfin ƴan sandan abun da yasa wasu daga cikinsu suka tsere bayan an ɗauki lokaci suna musayar wuta.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...