Ƴan Bindiga Sun Sace Wani Babban Limami

Wasu da ake zargin yan bindiga ne sun sace Ibrahim Bodunde Oyinlade babban limamin garin Uso dake karamar hukumar Owo ta jihar Ondo.

Kamfanin Dilllancin Labarai na Najeriya NAN ya rawaito cewa an sace limamin mai shekaru 67 a gonarsa dake sansanin Asolo da tsakar ranar Asabar.

Wata majiya dake iyalinsa ta ce sun kai rahoton bacewarsa gurin yan sanda bayan da ya kai ƙarfe biyu bai dawo gida ba kuma wayarsa ba a daga wa.

“Masu garkuwar sun tuntubi iyalinsa amma har yanzu basu bukaci kuɗin fansa ba,”ya ce.

Da ta ke tabbatar da faruwar lamarin, Olufunmilayo Odunlami-Omisanya mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ta ce yan sanda da kuma yan bijilante suna bincike dazuka don neman limamin.

Odunlami ta ce an gano waya da kuma motar limamin a gonar.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...