Ƴan bindiga sun sace tsohon ɗan takarar gwamnan Filato

Rahotanni daga jihar Filato a Najeriya na cewa ƴan bindiga sun sace tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Filato a zaɓen 2019, Nkemi Nicholas Nashe.

Mista Nashe wanda jigo ne a Jam’iyyar PDP, ya taɓa riƙe muƙamin Shugaban Ƙaramar Hukumar Shendam a baya.

Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito cewa wani makusancin Mista Nshe ɗin na cewa jama’ na zaman ɗar-ɗar tun bayan faruwar wannan lamari a Shendam.

Shi kansa gwamnan jihar mai ci a yanzu Simon Lalong ya fito ne daga Ƙaramar Hukumar Shendam.

Sace Mista Nshe na zuwa ne ƙwanaki kaɗan bayan sakin wani basarake a jihar ta Filato da aka sace, Charles Mato Dakat.

Sai dai sojoji da ke jihar sun bayyana cewa sun kama mutum takwas da suke zargi da hannu a sace basaraken.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...