Ƴan bindiga sun kashe mutane 9 ciki har da hakimi a wani ƙauye a Katsina

Wasu ‘yan bindiga sun sake kai hari da sanyin safiyar ranar Alhamis a kauyen Kuka Babangida da ke karamar hukumar Jibia ta jihar Katsina, inda suka kashe mutane akalla tara ciki har da hakimin kauyen, Idris Haruna.

Shugaban karamar hukumar Bashir Sabiu ya tabbatar da faruwar lamarin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Katsina, ASP Abubakar Aliyu, shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin.

Rahotanni sun nuna cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen ne ‘yan mintuna kadan kafin tsakar dare inda suka yi ta kai farmaki har zuwa karfe 1:30 na safiyar ranar Alhamis.

Mazauna kauyen sun ce ‘yan fashin sun dauki lokaci suna bi gida-gida suna neman wasu abubuwa masu daraja da suka hada da kudi.

Hat yanzu dai tsuguno bai ƙare ba a Arewacin Najeriya inda har yanzu ake samu tashe-tashen hankula da suka hada da satar mutane da kashe-kashe.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...