Kungiyoyin Kwadago na NLC da TUC a Najeriya sun dakatar da shirinsu na tafiya yajin aiki nan da wata daya.
Sun bayyana haka ne ranar Litinin da daddare, suna masu cewa gwamnatin tarayya ta kara N35,000 a albashin ma’aikatanta wanda za a soma biya daga watan Satumba.
Kungiyoyin dai sun fara maganar yakin aikin ne dai sanadiyyar wahala da ƴan Najeriya ke sha saboda cire tallafin man fetur da kuma wasu al’amurra.