Ƙasar Nijar Ta Ƙaddamar Da Sabon Katin Shaidar Ɗan Ƙasa



Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ƙaddamar da sabon katin shaidar zama ɗan ƙasa, da nufin ƙarfafa tsaro da kuma zamanantar da tsarin tantance jama’a.

An fara aiwatar da shirin ne a birnin Yamai, a ofishin ƴan sanda na Yantala.

Hukumomi sun bayyana cewa wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarin ƙasashen yankin Sahel na inganta musayar bayanai da sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a tsakanin ƙasashen mambobin ƙungiyar.

Sabon katin zai zama wajibi ga dukkan ƴan ƙasa da suka kai shekaru 15 zuwa sama.

More from this stream

Recomended