
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ƙaddamar da sabon katin shaidar zama ɗan ƙasa, da nufin ƙarfafa tsaro da kuma zamanantar da tsarin tantance jama’a.
An fara aiwatar da shirin ne a birnin Yamai, a ofishin ƴan sanda na Yantala.
Hukumomi sun bayyana cewa wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarin ƙasashen yankin Sahel na inganta musayar bayanai da sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a tsakanin ƙasashen mambobin ƙungiyar.
Sabon katin zai zama wajibi ga dukkan ƴan ƙasa da suka kai shekaru 15 zuwa sama.