
Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya bada umarnin gaggauta hana sayar da man fetur a gidajen mai a fadin karamar hukumar Bama ciki har da garin Bama da Banki.
Bama tana yankin arewa maso gabashin jihar Borno inda tayi iyaka da kasar Chad da kuma kasar Kamaru.
Hanin wanda aka sanar da shi bayan cikakkiyar tattaunawa da jami’an tsaro a jihar an yi shine domin magance kalubalen tsaro dake addabar jihar.
Mai bawa gwamna shawara kan kafafen yada labarai, Dauda Iliya a wata sanarwa ranar Asabar ya ce matakin wani bangare ne na dabara da shiri na tunkarar kalubalen yan ta’adda a jihar.
Ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu yana karya dokar to zai fuskanci hukunci.