‘Yan Sanda Za Su Gurfanar Da Mutane 4 Kan Rikicin Da Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 8 A Kebbi



Rundunar ’yan sandan jihar Kebbi ta tabbatar da kama mutane 4 da ake zargi da hannu a rikicin manoma da makiyaya da ya faru a garin Gulma da ke ƙaramar hukumar Argungu.

Rundunar ta ce rikicin ya yi sanadin mutuwar mutane 8, kuma za a gurfanar da waɗanda aka kama a gaban kotu nan ba da jimawa ba.

Kakakin rundunar, Bashir Usman, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis.

Rahotanni sun ce rikicin ya fara ne bayan zargin wani makiyayi Bafullatani da kashe wani manomi da wuƙa a gonarsa, lamarin da ya jawo ramuwar gayya daga wasu manoma da suka kai hari wasu matsugunan Fulani.

’Yan sandan sun bayyana sunayen waɗanda aka kama da suka haɗa da Musa Makera, Saidu Adamu, Shafi’u Hamza da Adamu Madugu.

Rundunar ta ce za a gurfanar da su kan zargin haɗa baki wajen aikata laifi, taro ba bisa ka’ida ba da kuma kisan kai.

Ta kuma ce bincike na ci gaba, yayin da jami’an tsaro ke ƙoƙarin cafke sauran waɗanda ake zargi da hannu a rikicin.

More from this stream

Recomended