Yan majalisar wakilai 173 na goyon bayan Gbajabiamiala

Wasu zaɓaɓɓun y’an majalisar wakilai ta tarayya su 173 da aka zaba karkashin jam’iyu daban-daban sun goyi bayan, shugaban masu rinjaye na majalisar, Femi Gbajabiamiala domin ya zamo kakakin majalisar wakilai.

Da yakewa manema labarai jawabi a Abuja,mai magana da yawun yan majalisar,Onofiok Luke dan jam’iyar PDP daga jihar Akwa Ibom ya bayyana cewa goyon bayan Gbajabiamiala ya zama shugaban majalisar ya samu sahalewar yan majalisa da suka fito daga jam’iyu daban-daban.

“Wannan kungiyar ta zababbun yan majalisu da aka zaba karkashin tutar jam’iyu daban-daban a yau mun yanke shawarar goyon bayan Femi Gbajabiamiala a matsayin kakakin majalisar wakilan tarayya ta 9.” ya ce.

Tunda farko jam’iyar APC ta yanke shawarar cewa yankin kudu maso gabas ne zai samar da kakakin majalisar wakilai kuma Gbajabiamiala ne dantakarar da take goyon bayan dadewa kan muƙamin.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar ɗaliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar ƙyanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen Ɗan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen ɗan fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...