Wasu zaɓaɓɓun y’an majalisar wakilai ta tarayya su 173 da aka zaba karkashin jam’iyu daban-daban sun goyi bayan, shugaban masu rinjaye na majalisar, Femi Gbajabiamiala domin ya zamo kakakin majalisar wakilai.
Da yakewa manema labarai jawabi a Abuja,mai magana da yawun yan majalisar,Onofiok Luke dan jam’iyar PDP daga jihar Akwa Ibom ya bayyana cewa goyon bayan Gbajabiamiala ya zama shugaban majalisar ya samu sahalewar yan majalisa da suka fito daga jam’iyu daban-daban.
“Wannan kungiyar ta zababbun yan majalisu da aka zaba karkashin tutar jam’iyu daban-daban a yau mun yanke shawarar goyon bayan Femi Gbajabiamiala a matsayin kakakin majalisar wakilan tarayya ta 9.” ya ce.
Tunda farko jam’iyar APC ta yanke shawarar cewa yankin kudu maso gabas ne zai samar da kakakin majalisar wakilai kuma Gbajabiamiala ne dantakarar da take goyon bayan dadewa kan muƙamin.