Yan majalisar dokokin jihar Taraba sun koma jam’iyyar APC daga PDP

John Bonzena  shugaban majalisar dokokin jihar Taraba ya sauya sheka daga jam’iyar PDP ya zuwa APC.

Sauya shekar ta gudana ne a ranar Litinin gabanin shirin sauya shekar da gwamnan jihar, Agbu Kefas ke yi na komawa jam’iyar ta APC.

Suma sauran masu rike da mukamai a majalisar dukkansu sun bi sawun shugaban majalisar wajen komawa jam’iyar ta APC daga PDP.

Wani fefan bidiyo da ya karade kafafen soshiyal midiya ya nuna yadda yan majalisar ke sauya hularsu ya zuwa hula mai dauke da alamar tafiyar siyasar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Bidiyon ya kuma nuna yan majalisar dauke da tsintsiya dake zama alamar jam’iyar APC.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]