Yan bindiga sun yi garkuwa da wani jami’in gidan gwamnatin Taraba – AREWA News

Wasu yan bindiga sun yi garkuwa da Danlami Yunana mataimakin daraktan harkokin gudanarwa a gidan gwamnatin jihar Taraba.

An yi garkuwa da Yunana a gidansa dake Magami a Jalingo da tsakar daren ranar Laraba.

Blessing Samuel,yar uwar mutumin wacce ta tabbatar faruwar lamarin ta ce yan bindigar sun yi dirar mikiya a gidan a tsakanin karfe daya zuwa biyu na dare.

Ta ce bayan da suka haura katangar gidan sun bude kofa da karfin tuwo.

“Su da yawa suka zo inda suka rika harbin kofar shiga cikin gidan domin samun damar shiga,” ta ce.

Wata majiyar dake iyalansa ta bayyana cewa tuni masu garkuwar suka bukaci a biyasu miliyan ₦50 a matsayin kudin fansa.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]