Yan bindiga sun yi garkuwa da wani jami’in gidan gwamnatin Taraba – AREWA News

Wasu yan bindiga sun yi garkuwa da Danlami Yunana mataimakin daraktan harkokin gudanarwa a gidan gwamnatin jihar Taraba.

An yi garkuwa da Yunana a gidansa dake Magami a Jalingo da tsakar daren ranar Laraba.

Blessing Samuel,yar uwar mutumin wacce ta tabbatar faruwar lamarin ta ce yan bindigar sun yi dirar mikiya a gidan a tsakanin karfe daya zuwa biyu na dare.

Ta ce bayan da suka haura katangar gidan sun bude kofa da karfin tuwo.

“Su da yawa suka zo inda suka rika harbin kofar shiga cikin gidan domin samun damar shiga,” ta ce.

Wata majiyar dake iyalansa ta bayyana cewa tuni masu garkuwar suka bukaci a biyasu miliyan ₦50 a matsayin kudin fansa.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...