Wasu yan bindiga sun yi garkuwa da Danlami Yunana mataimakin daraktan harkokin gudanarwa a gidan gwamnatin jihar Taraba.
An yi garkuwa da Yunana a gidansa dake Magami a Jalingo da tsakar daren ranar Laraba.
Blessing Samuel,yar uwar mutumin wacce ta tabbatar faruwar lamarin ta ce yan bindigar sun yi dirar mikiya a gidan a tsakanin karfe daya zuwa biyu na dare.
Ta ce bayan da suka haura katangar gidan sun bude kofa da karfin tuwo.
“Su da yawa suka zo inda suka rika harbin kofar shiga cikin gidan domin samun damar shiga,” ta ce.
Wata majiyar dake iyalansa ta bayyana cewa tuni masu garkuwar suka bukaci a biyasu miliyan ₦50 a matsayin kudin fansa.