Yan bindiga sun yi garkuwa da wani jami’in gidan gwamnatin Taraba – AREWA News

Wasu yan bindiga sun yi garkuwa da Danlami Yunana mataimakin daraktan harkokin gudanarwa a gidan gwamnatin jihar Taraba.

An yi garkuwa da Yunana a gidansa dake Magami a Jalingo da tsakar daren ranar Laraba.

Blessing Samuel,yar uwar mutumin wacce ta tabbatar faruwar lamarin ta ce yan bindigar sun yi dirar mikiya a gidan a tsakanin karfe daya zuwa biyu na dare.

Ta ce bayan da suka haura katangar gidan sun bude kofa da karfin tuwo.

“Su da yawa suka zo inda suka rika harbin kofar shiga cikin gidan domin samun damar shiga,” ta ce.

Wata majiyar dake iyalansa ta bayyana cewa tuni masu garkuwar suka bukaci a biyasu miliyan ₦50 a matsayin kudin fansa.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]